Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yajin Aikin Ma’aikatan Majalisun Najeriya Ya Shiga Rana Ta Hudu


Yajin aikin kungiyar ma'aikatan majalisun dokokin Najeriya.
Yajin aikin kungiyar ma'aikatan majalisun dokokin Najeriya.

Yau aka shiga rana ta huku da kasancewar zauruka da harabobin majalisun dokokin jihohin Najeriya 36 a garkame, biyo bayan yajin aikin da kungiyar ma’aikatan majalisun ke yi, akan batun aiwatar da dokar tabbatar da ‘yancin gashin kai ta fuskar kudade da ma’aikata.

Gabanin tsunduma wannan yajin aiki na sai baba ya gani, sai da shugabancin kungiyar na kasa baki daya ya yi gargadin makonni uku a karon farko kana ya kara makamancin sa na tsawon makonni biyu.

A hirar sa da Muryar Amurka, Comrade Ubale Yusuf, shugaban kungiyar ma’aikatan majalisun dokokin Najeriya reshen jihar Kano ya bayyana cewa, za su ci gaba da rufe majalisun har zuwa lokacin da za a samu daidaito bisa ga umarnin da su ka samu daga shugabannin kungiyar na kasa.

Yajin aikin kungiyar ma'aikatan majalisun dokokin Najeriya
Yajin aikin kungiyar ma'aikatan majalisun dokokin Najeriya

Shi kuwa takwaransa na jihar Jigawa, comrade Umar Adamu Kazaure cewa yake yajin baya nufin kassara ayyukan majalisar dokoki a jihohi. Bisa ga cewarsa, sun shiga yajin aikin ne domin karfafa aikin majalisa. Yace aikin majalisar shine, kafa doka, idan kuma za a kafa doka a samu wani bangare a kasar yana keta dokar ya nuna ke nan ana yi wa aikin majalisar zagon kasa.

Karin bayani akan: Jihar Kano, majalisun dokokin najeriya​, Nigeria, da Najeriya.

Yanzu haka dai kungiyoyin rajin shugabanci na gari a Najeriya sun fara tsokaci akan wannan batu.

Da yake tsokaci kan lamarin, Comrade Abdulrazak Alkali guda cikin ‘yan gwagwarmayar shugabanci na gari a Najeriya ya bayyana cewa, ba alfarma wani zai yi wa majalisun ba, amma doka ce ta tsara a basu kudaden gudanar da ayyukansu kai tsaye daga matakin tarayya.

Hatimin ikon alkali
Hatimin ikon alkali

Bisa ga cewarsa, kungiyarsu ta tunkari majalisun jihohi da dama inda suka shawarcesu su tabbatar sun ci moriyar wannan doka da shugaban kasa ya jadada cewa lallai a gudanar da wannan dokar.

A nasa banagaren, Sanata Mas’udu Eljibril Doguwa wakili a majalisar dattawan Najeriya ya bayyana cewa, rashin aiki da duk wata dokar kasa abin kyama ne.

Saurari cikakken rahoton Mahmud Ibrahim Kwari cikin sauti:

Yajin Aikin Ma’aikatan Majalisun Najeriya Ya Shiga Rana Ta Hudu-3:30"
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:31 0:00


  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG