Mayakan Boko Haram sun kai wani sabon hari wanda ya halaka jandarmomi 2 a garin Sagieme dake karamar hukumar potokol a jihar arewa mai nisa inda suka kwashe awowi kusan biyu suna batakashi.
A garin Sagieme gungun maharani na Boko Haram, sun bude wuta a wani ofishin ‘Jandarmomi Sagieme, inda akayi dauki musayan wuta a tsakaninsu, wanda yayi sanadiyar mutuwar jandarmomi biyu.
Rahotani na nuni da cewa maharani Boko Haram, sun shiga garin ne da misalign bakwai da rabi ne a cikin wata mota da kuma Babura biyu inda daga bisani da jandarmomin suka ranta ana kare.
Maharan na Boko Haram dai na shiga kasar ta Kamaru ne ta kan iyakar kasar da tarayyar Najeriya. Muryar Amurka ta nemi jin ta bakin gwamnan jihar arewa mai nisa Mijinyawa mai nisa amma abin ya ci tura.
Facebook Forum