Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

‘Yan Habasha Mazauna Amurka Sun Yi Zanga-zanga Kan Kisan Hachalu


'Yan Habasha Sun Yi Zanga-zanga Kan kisan Hachalu a Amurka
'Yan Habasha Sun Yi Zanga-zanga Kan kisan Hachalu a Amurka

Kusan mako biyu bayan kisan gillar da aka yi wa wani fitaccen mawaki a kasar Habasha, dubban ‘yan kasar mazauna Amurka da kuma wasu kasashen sun nuna jimamin mutuwar mawakin ta hanyar gudanar da zanga-zangar lumana domin nuna fushinsu ga hukumomin Addis Ababa.

A birnin Minneapolis da ke Minnesota, jihar da aka fi samun ‘yan kabilar Oromo, mutum akalla 1,500 suka datse wata babbar hanya har sama da sa’a guda a karshen makon da ya gabata.

Mutuwar mawaki Hachalu Hundessa dan shekara 34 da haihuwa, wanda aka harbe har lahira a Addis Ababa a ranar 29 ga watan Yuni, ta sa ‘yan kabilar ta Oromo sun hada kai domin nuna adawarsu ga Firai Ministan Habasha Abiy Ahmed.

Taron Addu'o'i Don Mawaki Hachalu Hundessa
Taron Addu'o'i Don Mawaki Hachalu Hundessa

A farkon watannan nan, a yayin wata hira da Muryar Amurka ta yi da Farfesa Henok Gabisa na jami’ar nazarin aikin Shari’a da ake kira Lee University, ya kwatanta wake-waken Hachalu a matsayin na “juyin juya hali.”

An dai yi ta zanga-zanga a sassan kasar Habasha bayan kisan mawakin, wacce ta sa aka yi fito-na-fito da jami’an tsaro.

Hukumomin kasar sun ce an kama kusan mutum 5,000 sannan wasu 239 sun mutu sanadiyyar zanga-zangar. Lamarin ya kai ga har sai da aka katse hanyoyin sadarwar yanar gizo a wani mataki don kwantar da tarzomar.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG