Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

'Yan Jarida A Plato Sun Sha Alwashin Bada Gudummuwa Ga Nasarar Zabe


Tambarin Hukumar Zaben Najeriya
Tambarin Hukumar Zaben Najeriya

‘Yan jarida a jahar pilato sun tunatar da kansu kan muhimmancin gabatar da rahotanni da zasu hana tada husuma a lokaci zabubbuka da za’a gudanar a Najeriya.

A wani taron kara wa juna sani da cibiyar sasantawa ta Humanitarian Dialogue ta shirya wa wakilan kafafen yada labarai daban-daban a jahar pilato, gabanin manyan zabubbuka dake karatowa a Najeriya, ‘yan jaridar sun ci alwashin gudanar da aikinsu bisa kundin tsarin aikin.

Jami’in cibiyar Humanitarian Dialogue, Ibrahim Sale Hassan yace sun shirya taron bitar wa ‘yan jaridan ne ganin yadda suke da muhimmaci wajen gudanar da zabe cikin tsanaki.

Jimi’in dake wayar da kan jama’a a hukumar zabe ta kasa dake jahar Pilato, Osaretin Imahiyereobo yayi amfani da dammar wajen shaida wa wadanda keda katunan zabe fiye da guda daya cewa ba zasu iya kada kuri’a ba.

Taron bitar mai taken gudunmowar ‘yan jarida wajen gudanar da zabe ba tare da tashin hankali ba, ya kuma tattauna kan gudunmuwan sauran masu ruwa da tsaki a harkar zabe zasu bayar wajen yin zabe ba tare da an kashe kowa ko lalata dukiya ba.

Saurari rahoton Zainab Babaji.

Bita kan aikin jarida-3:30"
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:32 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG