Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

'Yan Sanda Sun Hallaka 'Yan Ta'adda 2, Sun Kuma Ceto Mutane 7 Da Dabbobi 142 A Jihar Katsina


'Yan sandan Najeriya
'Yan sandan Najeriya

Tawagar rundunar 'yan sandan jihar Katsina ta yi nasarar dakile farmakin 'yan ta'adda masu yawa, wadanda ke tare mutane su yi musu fashi a titin Zango zuwa Kankara dake jihar ta Katsina,

Rundunar ta kuma yi nasarar kashe wani da ake zargi dan ta’adda ne da kuma kubuto da mutane takwas ciki har da kananan yara hudu da aka yi garkuwa da su.

Kazalika rundunar ta yi nasarar kwato shanu guda 82 da tumaki 70 da bindiga kirar AK-47 guda daya daga hannun yan ta’addan.

Kakakin 'yan sandan jihar, SP Gambo Isah, shi ya tabbatar da lamarin ga manema labarai a hedkwatar su dake Katsina a jiya Alhamis, inda aka bayyana wadanda aka ceto da gawar dan ta’addan da kuma bindigar da aka kwato.

Yan sandan Najeriya
Yan sandan Najeriya

Haka zalika, DPOn Kankara ya jagoranci tawagar 'yan sanda wajen dakile farmakin 'yan ta'addan dake addabar kauyen Fuloti da Gandu Karfi a karamar hukumar Malumfashi bayan samun kiran gaggawa daga mazauna yankin.

Bayan musayar wuta da 'yan ta'addan, 'yan sandan sun yi nasarar sheke daya daga cikin hatsabiban, bayan sun ceto mutane bakwai da aka yi garkuwa da su, wadanda suka hada da yara da mata masu shayarwa guda hudu.

XS
SM
MD
LG