Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

‘Yan Sanda Sunyi Nasarar Kashe Barayin Shanu A Jihar Bauchi.


Yan Bindiga Barayin Shanu A Zamfara
Yan Bindiga Barayin Shanu A Zamfara

Wakilin sashen sahen Hausa dake Bauchi Abdulwahab ya tattauna da Fulanin da suka ce barayin suna musu fashi da kuma kashe su

Ga kuma abinda daya daga cikin su yak e shaidawa Abdulwab din.

‘’Abinda ya faru shine kawu na Alhaji Kabo an zo an same shi da dansa wato kanina Kenan shi dan, an kashe su da bindiga ance su bada kudi Alhaji yace shi ba zai bada kudi ba.’’

Da Abdulwahab ya tambaye shi ko su wanene suka zo suka kashe shi? Sai yace.

‘’Su ‘yan miliyan Kenan suna barayin Kenan to daga baya satin da ya juyo wani makwabcin mu daga gabas sunan sa Musa Kurma shima an kashe shi, daga baya ma akwai wani saurayi dan gidan shugaba Tuggil shima an kashe shi, sai daga baya suka zo suka kashe Mani Bude, mutane 5 kenan wadanda aka kashe kusa damu banda kudaden da suka kakkarba, gaba daya sun tada muna hankali mun rasa inda zamu sa ran mu.’’

Fulanin da wadannan bayarin shanun suka addaba sunyi wa Abdulwahab bayani daban-daban.

Ga Abdulwahab Mohammed da ci gaban rahoton 5’17

please wait

No media source currently available

0:00 0:05:17 0:00

XS
SM
MD
LG