Shugaban yankin Catalonia, Carles Puidgemont, ya fada yau cewa, majalisar yankin zata kada kuri’ar ayyana 'yancin wannan yanki idan gwamnatin Spaniya taki tattaunawa a maimakon haka ta aiwatar da barazanarta ta kwace ‘yancin cin gashin kan da yankin ke da shi.
PM Mariano Rajoy yaba Pudgemont wa’adin zuwa safiyar yau alhamis ya bayyana ko ya riga ya ayyana ‘yanci a yankin bayan kuri’ar raba gardamar da aka kada farkon watan nan.
Puidgemont ya ayyana ‘yancin yankin a kaikaice a jawabin da ya gabatar makon da ya gabata, sai dai yace ya dakatar da daukar mataki a hukumance domin bada damar tattaunawa da gwamnati a birnin Madrid. Ya bayyana matsayinsa a wata wasika da ya rubuta yau alhamis ana dab da cikar wa’adin da aka dibar masa.
Nan da nan ofishin Rajoy ya maida martani da cewa, yana shirin wani taron majalisar zartarwa na musamman ranar asabar da nufin aiwatar da sashe na dari da hamsin da biyar na kundin tsarin mulkin kasar Spain da yaba gwamnati janye ikon cin gashin kan yankin.
Masu kada kuri’a a Cataloniya sun zabi ‘yantar da yankin a zaben raba gardamar da aka gudanar ranar daya ga watan Oktoba, sai dai kasa da rabin wadanda suka cancanci kada kuri’a suka gudanar da zabe, yayinda masu adawa suka kauracewa zaben. Gwamnatin Rajo tayi watsi da kuri’ar raba gardamar da tace ta sabawa doka.
Facebook Forum