Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yaran Yan Gudun Hijiran Rohingya Sun Fara Samun Rigakafin Kwalara


President-elect Joe Biden, his wife Jill Biden and Vice President-elect Kamala Harris and her husband Doug Emhoff arrive at the steps of the U.S. Capitol for the start of the official inauguration ceremonies, in Washington, Wednesday, Jan. 20, 2021. (AP Photo/J. Scott Applewhite)
President-elect Joe Biden, his wife Jill Biden and Vice President-elect Kamala Harris and her husband Doug Emhoff arrive at the steps of the U.S. Capitol for the start of the official inauguration ceremonies, in Washington, Wednesday, Jan. 20, 2021. (AP Photo/J. Scott Applewhite)

A jiya Asabar ne aka fara aikin bada rigakfi cutar kwalara ga dubban kananan yaran yan kabilar Rohingya da suke gudun hijira Cox Bazar dake kasar Bangldesh a huska ta biyu.

Aikin bada rigakafin na Kolera ta baki da hukumar kiwon lafiya ta WHO ke jagoranta yana auna kusan kananan yara dubu dari da tamani yan tsakanin shekaru daya zuwa biyar. Yaran zasu samu Karin wani rigakafin da zai kare su daga wasu cututtuka.


Yaran sun samu maganin a karon farko da aka kaddamar da aikin bada rigakafin a ranar goma ga watan Oktoba da ta shige. A wannan lokacin an baiwa mutane sama da dubu dari bakwai rigakafin ta bakinsu wandanda suka haura shekara daya.

Kakakin hukumar WHO Tarik Jasarevic yace ma’aikatar lafiyar zasu kuma bada rigakafin cutar shan inna ga yara yan shekaru biyar a cikin wannan aikin don kare su daga cutar da zata nakasa su.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:24 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG