Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yau ake sa ran fara aiwatar da wani bangaren dokar hana wadansu kasashe shiga Amurka


Shugaban Amurka Donald Trump -Washington, DC, 28, 2017.
Shugaban Amurka Donald Trump -Washington, DC, 28, 2017.

Jami’an shige da ficen nan Amurka na jiran tsarin yadda zasu aiwatar da umurnin shugaba Donald Trump akan dokar hana mutanen wadansu kasashe zuwa Amirka, dokar da kila a kaddamar da fara amfani da ita da safiyar yau alhamis.

Jami’an ma’aikatar harkokin waje, dana Shari’a da kuma na tsaron Cikin gida kawo yanzu basu da cikakken dangane da wanda ya cancanci shigowa Amurka daga wadannan kasashan 6 da dokar ta shafa, wanene kuma bai cancanta ba.

Kasashen dai sun hada da Iran, Libya, Somalia, Sudan, Syria da kuma Yemen.

Ranar Litinin da ta gabata, babbar Kotun Amurka ta sake maido da wani bangaren dokar da wadansu kananan kotuna suka dakatar da farko, suna dogara ga abinda dokar kasa tace dangane da batun tsaro.

Kotun ta bada umurnin cewa sai an yi zama akan wannan batu, amma kafin nan bakin da za a bari su shigo sai sun nuna cewa suna da wadansu ‘yan uwa na kud-da-kud kafin a barsu su shigo kasar.

Sai dai kotun bata fayyace ma’anar wannan dangantakar ta kud-da kud ba.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG