Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yawan Hare-Hare Na Haifar Da Zaman Dardar a Mali


A yayin da kasar Mali ke fara zaman makoki na kwanaki uku a jiya Litinin, bayan da aka kashe mutane 54 a wani harin da aka kai a makon da ya gabata, mazauna yankin sun nuna fargaba game da karuwar tashe-tashen hankali, yayin da wasu manazarta suka yi kira da a kara kaimi wajen ayyukan tattara bayanan sirri da hadin kai.

Yayin da yake magana kan wannan hari, wanda aka kai a ranar Juma’ar da ta gabata, wani mai fafutuka da ake kira Dr. Abdoul Kane Diallo, ya ce "ba za mu zura ido muna kallo a kowacce rana mutane na kawo hari akan sansanoninmu ba, suna kashe daruruwan sojojinmu."

Diallo ya nuna fushinsa a fili, saboda a cewars shi, duk da cewa an sanar da hukumomi nan da nan a lokacin da aka kai harin da rana, "amma abin mamakin shi ne, babu wani dauki da aka kai."

Tuni dai kungiyar ‘yan ta’adda ta ISIS ta dauki alhakin kai harin.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG