Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Zaben Fidda gwanin Gwamnonin PDP Sun Yi Sabbin Fuskoki A Siyasar Jihohin Bauchi Da Gombe


Wani taron PDP da ta yi a baya (Instagram/PDP) an yi amfani da wannan hoto don nuna misali.
Wani taron PDP da ta yi a baya (Instagram/PDP) an yi amfani da wannan hoto don nuna misali.

Zaben fidda gwani na gwamnoni a Jam’iyar PDP a Jihohin Bauchi da kuma Gombe ya samar da sabbin fuskoki a fagen siyasa.

Tsohon Sakataren gwamnatin Jihar, Barrister Kashim Ibrahim shine aka zaba wanda zai yi takarar kujerar gwamna, a yayinda a Jihar Gombe aka zabi Muhammed Jibrin Barde wanda ya yi canjin sheka daga Jam’iyar APC.

Zaben fidda gwanin da ya gudana a Bauchi, ya gudana ne, ba tare da wata hamayya ba, wato kadaran kadahan, inda aka kada masa kuri’u guda dari shida da hamsin da biyar (655 ).

A jawabin da ya gabatar a bayan da aka bayyana sakamakon zaben, tsohon Sakataren gwamnatin Jihar, Barrister Kashim Ibrahim yace yana godiya ga mutanen da suka zabe shi don ganin ya cancanta.

Shima shugaban Jam’iyar PDP a Jihar Bauchi, Hamza Koshe Akuyam, yace jama’a sun zabi abinda suke so.

A Jihar Gombe, makwabciyar Bauchi, 'yan takarar guda biyar ne suka fafata a zaben fidda gwanin wanda daga karshe Alhaji Muhammed Barde Jibrin ya yi nasara da kuri’u dari da sittin (160). Shi dai wanda aka zaban masani ne kan harkokin kudi.

A wata sabuwa kuma, ‘ya’yan jam’iyar APC a jihar Bauchi, sun yi taro da kuma yin kira ga uwar jam’iyar ta kasa da kuma a jihar da su yi wa Allah su bari a yi zabe a maimakon dauki dora.

Saurari cikakken rahoton cikin sauti:

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:21 0:00
XS
SM
MD
LG