Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Zama Da Dan Masanin Kano, Tamkar Zama a Jami'a Ne- Ribadu


Tsohon shugaban EFCC, Mallam Nuhu Ribadu
Tsohon shugaban EFCC, Mallam Nuhu Ribadu

Shugabannin a Najeriya na ci gaba da yaba wa tare da mika ta'aziyyarsu bisa rasuwar tsohon Jakadan Najeriya a Majalisar Dinkin Duniya, Dan Masanin Kano, Alhaji Yusuf Maitama Sule, wanda ya rasu a farkon makon nan.

Tsohon shugaban hukumar dake yaki da masu yi wa tattalin arzikin zagon kasa ta EFCC, Mallam Nuhu Ribadu ya dora muryarsa a kan na masu yi wa marigayi Dan Masanain Kano kyakkaywan shaida yana mai cewa, Maitama Sule dattijo ne kuma abin koyi.

Ribadu ya ce zama da Dan Masanin Kano tamkar zama a jami’a ce saboda "za ka samu karuwa ta musamman kan batutuwan siyasa."

Da yake ci gaba da yabawa marigayin, tsohon shugaban na EFCC ya ce a duk lokaci da aka hadu da Dan Masanin Kano za ka ji sabon abu da zai kara maka ilimi.

Saurari rahoton nan domin jin karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:04 0:00

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG