Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Zelensky Ya Nemi Agajin Trump Bayan Dakatar Da Tallafi


A yau Talata, Shugaba Volodymyr Zelensky ya bayyana cewar yana bukatar daidaita al'amura tsakaninsa da Donald Trump tare da yin aiki karkashin jagorancinsa domin samar da dawammen zaman lafiya a ukraine.

A kalamansa na baina jama'a na farko tun bayan da Trump ya dakatar da tallafin sojan Amurka ga Ukraine, Zelensky ya nemi tsagaita wuta ta sama data ruwa a matsayin matakin farko na kawo karshen yakin shekaru 3 tare da yin alkawarin rattaba hannu akan yarjejeniyar hakar ma'adinai tsakaninsa da Washington.

Rushewar alakar Kyiv da Washington ta lokacin yaki ta bayyana a zahiri tun bayan arangamar cacar bakin data afku a ofishin shugaban Amurka tsakanin Zelensky da Trump a makon daya gabata, abinda ya janyo babbar kawar Ukraine dakatar da tallafin soja mai matukar mahimmanci.

"Ni da tawagata na cikin shirin yin aiki a karkashin jagorancin Shugaba Trump domin samun lafiya mai dorewa," kamar yadda Zelensky ya shafinsa Na X.

"Ganawarmu a Washington, a fadar White House a Juma'ar data gabata, bata gudana yadda ya dace ba," a cewar shugaban Ukraine. "lokaci yayi da zamu gyara al'amura su tafi daidai."

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG