Amurka da Rasha sun sake cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a Aleppo dake Syria

Yadda yaki ya ragargaza Aleppo

Amurka da Rasha sun cimma wata karamar yarjejeniyar tsagaita wuta a birnin Aleppo na kasar Syria, inda mummunan fadan da ake yi tsakanin gwamnati da ‘yan tawaye ya kashe fiye da farar hula 280 daga watan Afirilu.

Ma’aikatar harkokin wajen Amurka ce ta jaddada haka a jiya Laraba na tsagaita wutar a Aleppo da kewaye, wanda yarjejeniyar ta fara aiki a jim kadan bayan tsakar daren agogon kasar.

Gwamnatin Syria ta ce zata mutunta yarjejeniyar tsagaita wutar a Aleppo, amma sun ce yarjejeniyar ta tsawon sa’o’i 48 ce kadai. A wata sanarwar ‘yan adawar Syria sun ce ya kamata ace an tsagaita wutar gaba daya ne ba a wasu zababbun wurare ba.

Kamar yadda Kakakin ‘yan adawa Salem al-Meslet yace, in ba haka ba to kuwa ba inda wannan yarjejeniyar zata je. Jami’ai a nan Amurka sun ce, duk da yarjejeniyar akwai rahotannin da ke cewa ana fada a wasu wuraren.

To amma duk da haka, idan aka dubi rikicin gaba daya, an samu yar dan lafawa. Amurka da Rasha ke kokarin shiga tsakanin tsagaita wutar don a samu daidaito tun a watan Fabrairun shekarar nan.