An Bayyana Nigeria da Sunan 'Daya Daga Cikin Kasashen Afirka da Sugabanita ke Barnatar da Dukiyar Al'Umma

Matsalar cin hanci da karbar rashawa, da ingiza farashin kaya domin cin bakar riba, da badda sawun kudaden haram, da kin biyan kudin haraji a kan lokaci, na daga cikin abubuwan da yanzu ke addabar Nigeria.
Jami’an dake gudanar da binciken halin zaman al’umma dake aiki tare da Bankin ayyukan ci gaban kasa da na al’umma a Afirka, sun bayyana cewar kasashen Afirka sun yi asasar kusan Dala miliyan dubu sau dubu uku da miliyan dari hudu ($1.4Trillion) saboda matsalar cin hanci da karbar rashawa cikin shekaru Talatin da suka gabata. Kuma mafi yawan asarar kudaden anyi ne a dalilin cin hanci da karbar rashawa da yin sama da fadin da ‘yan kasuwa keyi, da hakan kuma ke janyo koma bayan ayyukan ci gaban kasa da na al’umma a jihohin Nigeria. Ana kuma iya cewa irin arziki da kudaden dake fita daga nahiyar Afirka a dalilin cin hanci da karbar rashawa su ne ke hana ayyukan ci gaban kasa.Zancen nan da ake yi irin wadancan kudaden da aka bayyana sun nunka har sau biyu a cikin shekaru da dama da suka gabata.