An Gayyaci Kim Jong Un Taron Kasashen Duniya

Vladimir Putin

Shugaban kasar Rasha Vladmir Putin ya gayyaci shugaban Koriya ta Arewa Kim Jong Un zuwa Rasha domin halartar wani taron kasashen duniya da za’ayi nan bada jimawa ba.

A yau litinin ne Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Rasha Dmitry Peskov ya shaidawa manema labarai a birnin Moscow cewa shugaba Putin ya aika wa shugaba Kim takartar gayyatar ne ta hanyar ministan harkokin wajen Rasha Sergei Lavrov a lokacin da ya kai ziyara Pyongyang a satin da ya gabata.

Peskov yace Putin ya bada shawarar Kim ya halarci taron tattalin arziki na kasashen Gabscin Turai da za a yi a birnin Vladivostok a watan Satumba mai zuwa.