BORNO: Jama'a Na Ganin Canjin da Shugaban Kasa Yayi Zai Kawo Lafiya

Shehun Borno Alhaji Muhammad Al-Amin ibn Al-Kanemi

Yawancin mutanen da suka bayyana ra'ayoyinsu suna ganin Allah ne ya kaddara cewa shugaban Najeriya zai kawo canjin kuma sun godewa Allah da fatan wannan shi ne zai kawo zaman lafiya

Addu'ar yawancin mutanen shi ne Allah ya tabbatar masu da zaman lafiya wannan karon, canjin ya zamar masu da alheri.

Akwai wasu kuma da suka yi farin ciki da sauyin. Wani yace suna jin dadi da sauyin da aka yi. Addu'ar ita ce Allah ya taimaka da nufin sauyin zai kawo zaman lafiya.

Wani ya ce saukar da jami'an tsaon ma kansa wata isakar lafiya ce ta kado. Suna fata sun kama hanyar samun zaman lafiya ke nan musamman idan shugabannin da aka nada sun tsare gaskiya tare da riketa.

Ga rahoton Haruna Dauda Biu.

Your browser doesn’t support HTML5

BORNO: Jama'a Na Ganin Canjin da Shugaban Kasa Yayi Zai Kawo Lafiya - 2' 12"