Labaran Wassanin VOA Hausa na ran 23 ga watan Yuni, 2014, Kofin Duniya, Ghana

  • Aliyu Mustapha

John Boye, Ghana

Shirin zai duba matsayin dukkan kasashe bayan wassani bibbiyu, zargin cuku-cuku a Ghana da kuma ‘yan wasan da kasashen suka dogara a kansu kacokan.

A yanzu dai kowace kasa ta buga wassani bibbiyu a gasar Cin Kofin Duniya da ake gudanarwa a Brazil, saboda haka yanzu kowacce ta san matsayinta. Wasu sun zarce, wasu kuma ana harramar komawa gida. Yayinda wannan ke faruwa kuma, a Ghana wata sabuwa ta bullo bayanda aka bankado cewa wasu jami’an hukumar kwallo ta GFA sun nemi toshiyar baki don su rinka barin ana cin Ghana a kwallon da take bugawa da wasu kasashe. Bayan wannan,zamuji ra’ayoyin wasu akan ko wadanne ‘yan wasa ne da, in babu su, zai yi wa kasashensu wuyar cin kwallo?

Your browser doesn’t support HTML5

Labaran Wassanin VOA Hausa, Kofin Duniya, Ghana - 12'40"