Majalisar Dinkin Duniya Zata Sake Nazarin Tsaro A dukkan Ofisoshinta

Babban magatakardan majalisar Dinkin Duniya Ban ki-moon.

Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Banki Moon yace Majalisar Dinkin Duniya zata yi nazarin barazanar matakan tsaro a dukkan ofisoshinta. Majalisar zata dauki wannan matakin ne a saboda harin bam din da aka kai ofishinta dake Abuja babban birnin taraiyar Nigeria.

Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Banki Moon yace Majalisar Dinkin Duniya zata yi nazarin barazanar matakan tsaro a dukkan ofisoshinta. Majalisar zata dauki wannan matakin ne a saboda harin bam din da aka kai ofishinta dake Abuja babban birnin taraiyar Nigeria.

A jiya talata Mr Ban ya fadawa kwamitin sulhu na Majalisar cewa Majalisar Dinkin Duniya zata yi nazarin harin da aka kai da kuma yin nazarin irin wannan barazana a duk fadin duniya.

Yace a filli yake cewa ‘yan ta’ada suna kara auna ofisoshin Majalisar da ma’aikatanta wajen kai hare hare. Yace mutane goma sha daya daga cikin ashirin da uku da aka kashe a Abuja ma’aikatan Majalisar ne.

Fiye da mutane tamanin ne suka ji rauni, a lokacinda wani mai harin kunar bakin wake ya kutsa kofofin fita na Majalisar ya shiga harabar ya aikata wannan danyen aikin.

-