Shugaban Nijer Ya Jaddada Kudirinsa Na Magance Matsalar Cin Hanci A Kasar

Shugaban kasar Nijer ya jaddada aniyar karfafa matakan yaki da cin hanci da karbar rashawa ta yadda za a soma hukunta wadanda aka kama da hannu a irin wannan haramtacciyar dabi’a dake zama ruwan dare a Nijer kamar sauran kasashen Afrika.

Mohamed Bazoum ya bukaci ‘yan kasar su ba shi lokaci kadan domin zartar da wannan mahimmin kudiri na kwatowa kasa hakkokinta daga hannun barayin biro kamar yadda ya bayyana wa shugaban sashen Hausa Aliyu Mustapha Sokoto.

Shugaban Nijer yace babu shakka kasashen Afrika na fama da wannan matsala ta cin hanci matsalar da ya kudiri aniyar magancewa a Nijer.

Bazoum Mohamed yace ba a fuskantar cin hanci a fannin ma’adanan karkashin kasa sakamakon matakan dake gudanar da wannan fanni amma matsalar ta shafi akasarin fannoni daga jami’an tsaro zuwa fannin ilimi, lafiya, haraji. da dai sauransu.

Saurari cikakken rahoton a cikin sauti:

Your browser doesn’t support HTML5

Shugaban Nijer Ya Jaddada Kudirinsa Na Magance Matsalar Cin Hanci A Kasar

Babban Kalubalen Da Na Fuskanta A Watanni 7 – Shugaba Bazoum

Your browser doesn’t support HTML5

Babban Kalubalen Da Na Fuskanta A Watanni 7 – Shugaba Bazoum

Nijar Na Bukatar Amfani Da Kudin Bai-Daya Da Najeriya – Shugaba Bazoum

Your browser doesn’t support HTML5

Nijar Na Bukatar Amfani Da Kudin Bai-Daya Da Najeriya – Shugaba Bazoum

Juyin Mulki A Guinea Bai Zo Da Mamaki Ba – Shugaba Bazoum

Your browser doesn’t support HTML5

Juyin Mulki A Guinea Bai Zo Da Mamaki Ba – Shugaba Bazoum