Sudan ta ayyana Sudan ta Kudu a matsayin mai kinta

  • Ibrahim Garba

Dubban 'yan gudun hijirar da rikicin Sudan ya rutsa da su.

Majalisar dokokin kasar Sudan ta ayyana Sudan ta kudu

Majalisar dokokin kasar Sudan ta ayyana Sudan ta kudu a zaman mai kin kasar Sudan wadda ke nuna kiyayyarta a fili a dai dai lokacin da rikici ke ci gaba da ta’azzara a kan iyakar kasashen biyu.

Bayan ‘yan majalisar dokokin Sudan sun kada kuri’ar jiya litinin a birnin Khartoum, sai shi kuma Ministan yada labrun Sudan ta kudu.

Barnaba Marial Benjamin ya bada sanarwar yin watsi da ayyanawar ta Sudan yace holoko ce kawai,domin ba yadda kasar Sudan ta kudu zata kasance mai gaba da kasar Sudan.