Tattauna Hanyoyin Yaki da Talauci a Najeriya a Taron Kasa Zai fi Amfani

Nigeria National Assembly

Kungiyar hada kan arewacin Najeriya tace tattauna hanyoyin yaki da talauci a Najeriya a taron kasa zai fi amfani
Kungiyar hada kan matasan arewacin Najeriya tace tattauna hanyoyin yaki da talauci a Najeriya, a taron kasa zai fi amfani ga al'umar Najeriya.

Shugaban, kungiyar Hassan Waziri Chinade ne ya furta haka a wata hira da yayi da wakilin Muryar Amurka, Nasiru Adamu El-Hikaya.

Yace yankin arewacin Najeriya, yafi sauran yankunan kasar yawan matasa, masu karancin ilimi da kuma karin talauci.

Wanda a cewarsa baida alfanu ga kasar, domin rashin ilimi da kuma talauci shike sa matasa fadawa aikata abubuwan da basu dace ba.

A wani labarin kuma Igwe Martins na yankin Ibo yayi watsi da masu dawo da kamfe din raba kasa ko kuma kafa kasar Biafra.

Your browser doesn’t support HTML5

Taron kasa na Abuja -3'32"