‘Yan Najeriya da dama sun yi ta korafi kan yadda ake samun karin tabarbarewar al’amaru a kasar, wadanda suka hada da karancin man fetur, wutar lantarki, rashin tsaro da kuma tabarbarewar tattalin arziki.
Shugaban Buhari ya amince da dokar zabe da aka yi wa kwaskwarima da za ta ba da damar yin amfani da na'urar tantance sakamakon zabe a zaben 2023 a wani yunkuri na yi wa zaben garambuwal.
Kungiyar tarayyar Afirka ta kammala taron ta na kwanaki biyu a hedikwatar birnin Addis Ababa dake kasar Ethiopia, tare da yanke muhimman shawarwari.
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa-EFCC, ta damke Shugaban gidan radiyon Muryar Nijeriya Mr. Okechuku Osita da zargin badakala da cin hanci da yakai Naira miliyan dubu’daya da miliyan ‘dari biyu ta aringizon kwangiloli da baiwa ‘yan uwansa ayyukkan boge.
“Muhimmancin wannan taro shi ne don a hada kai tsakaninmu da su, don a ci moriyar irin ci gaban da Turkiyya take samu," in ji Garba Shehu.
Shugaban kasa Muhammadu Buhari da Shugaban kasa Cyril Ramaphosa sun kaddamar da taron tattaunawa tsakanin matasan Najeriya da Afirka ta Kudu ranar Alhamis a Abuja, don samar da zaman lafiya da tsaro, ci gaban matasa da kuma shiga harkokin siyasa.
Shugaban Nigeria Muhammadu Buhari ya isa ‘kasar Saudiyya domin halartar taron saka jari domin bunkasa rayuwar al’umma.
Wasu masu sharhi na ganin rashin baiwa mataimakin shugaban kasa daman rike kasar yayin da shugaban ke duba lafiyarsa a Ingila, ka iya shafar dangantakarsu.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya gana da hafsoshin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki a harkokin tsaro na Najeriya gabanin ya kama hanyarsa ta zuwa London don gain likita.
Gwamnatin Nigeria ta ba da umurnin hana hakar zinari da sauran albarkatun ‘kasa a jihar Zamfara tare da haramta shawagin jiragen sama a sararin samaniyar jihar A kokarin yaki da ta’ adds ci ya yayi kamari a jihar.
Gwamnonin arewacin Najeriya sun dukufa wajen neman hadin kan gwamnatin tarayya, don kafa rugage da wuraren kiwo domin hana Fulani yawon kiwo da ke sanadin tashe tashen hankula.
Najeriya ta bi sahun sauran kasashen duniya wajen tsananta matakan dakile yaduwar cutar corona, yayin da ita kuma cutar ke kara barazana tare da neman rikida a wasu kasashen.
Biyo bayan ceto daliban makarantar sakandaren garin Kankara da aka yi bayan da aka sace su a 'yan kwanakin da suka gabata, yanzu hankali ya koma akan yadda kwararru zasu taimaka wa daliban warwarewa da matsalar fargaba da firgita.
A daidai lokacin da Majalisar Wakilan Najeriya ke jiran bayyanar shugaban kasa gabanta yau Alhamis, domin amsa tambayoyi game da halin tabarbarewar tsaro da kasa ke ciki, Ministan Shari’a ya ce bayanin Buhari ga Majalisa na iya amfanar ‘yan bindiga
A cigaba da lalubo mafita game da matsalolin tsaro da rayuwa a Najeriya, Shugaba Muhammadu Buhari ya jagoranci taron masu ruwa da tsaki, inda ya ciza ya kuma hura.
Yayin da Najeriya ke bukin zagayowa ta 60 ta ranar samun 'yancin kanta a cikin wani yanayi na matsalolin tsaro, tattalin arziki da kuma annobar COVID-19, Shugaba Buhari ya ce muddun aka hada kai za a kai ga gaci.
Shugaban kwamitin Shugaban Nigeria Mai binciken badakalar da ake zargin Mustafa Ibrahim Magu ya tafka a hukamar yaki da cin hanci da rashawa, Justice Ayo Salami ya karyata labarin da lauyoyin Magu suka yada na cewar wai yayi nadamar kar’bar aikin.
Domin Kari