WASHINGTON, DC —
Wani jami'in fadar shugaban Amurka ta white House, ya ce a wani matakin jajantawa ma'aikatan gwamnatin tarayya wadanda zasu yi hasarar wani bangare na albashinsu ala tilas, shugaba Barack Obama yace shi ma zai mayarwa da gwamnati kashi 5 cikin 100 na albashinsa.
Jami'in ya fada yau laraba cewa shi ma shugaba Obama ya yanke shawarar sadaukar da kai irin wanda ala tilas wasu ma'aikatan gwamnati zasu yi a saboda dokar nan da ta tilasta zabtare kudaden da kowace ma'aikata da hukuma ta gwamnatin tarayya a nan Amurka ta ke kashewa.
Shugaba Obama yana samun albashin Dala dubu 400 a kowace shekara, kafin a cire haraji daga ciki. Kashi biyar na albashin nasa da zai sadaukar daga ranar 1 ga watan Maris, lokacin da wannan doka ta fara aiki, na nufin cewa a kowane wata zai mayar da kimanin dala dubu daya da dari bakwai.
A ranar talata ma, sakataren tsaron Amurka, Chuck Hagel, da mukaddashinsa Ashton Carter, duk sun ce su ma zasu maidawa gwamnatin wani bangare na albashinsu a matsayin wani matakin jajantawa ma'aikatansu da zasu yi hasarar wani bangare na albashinsu.
Jami'in ya fada yau laraba cewa shi ma shugaba Obama ya yanke shawarar sadaukar da kai irin wanda ala tilas wasu ma'aikatan gwamnati zasu yi a saboda dokar nan da ta tilasta zabtare kudaden da kowace ma'aikata da hukuma ta gwamnatin tarayya a nan Amurka ta ke kashewa.
Shugaba Obama yana samun albashin Dala dubu 400 a kowace shekara, kafin a cire haraji daga ciki. Kashi biyar na albashin nasa da zai sadaukar daga ranar 1 ga watan Maris, lokacin da wannan doka ta fara aiki, na nufin cewa a kowane wata zai mayar da kimanin dala dubu daya da dari bakwai.
A ranar talata ma, sakataren tsaron Amurka, Chuck Hagel, da mukaddashinsa Ashton Carter, duk sun ce su ma zasu maidawa gwamnatin wani bangare na albashinsu a matsayin wani matakin jajantawa ma'aikatansu da zasu yi hasarar wani bangare na albashinsu.