Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaba Barack Obama Ya Rage Ma Kansa Albashi


Shugaba Obama da shugaban ma'aikatan fadarsa, denis McDonough, cikin ofishin shugaban. An dauki hoton ranar 6 Fabrairu 2013.
Shugaba Obama da shugaban ma'aikatan fadarsa, denis McDonough, cikin ofishin shugaban. An dauki hoton ranar 6 Fabrairu 2013.

Shugaban na Amurka yace zai mayarwa da gwamnati kashi 5 cikin 100 na albashinsa don jajantawa ma'aikatan da zasu yi hasarar wani bangaren albashinsu

Wani jami'in fadar shugaban Amurka ta white House, ya ce a wani matakin jajantawa ma'aikatan gwamnatin tarayya wadanda zasu yi hasarar wani bangare na albashinsu ala tilas, shugaba Barack Obama yace shi ma zai mayarwa da gwamnati kashi 5 cikin 100 na albashinsa.

Jami'in ya fada yau laraba cewa shi ma shugaba Obama ya yanke shawarar sadaukar da kai irin wanda ala tilas wasu ma'aikatan gwamnati zasu yi a saboda dokar nan da ta tilasta zabtare kudaden da kowace ma'aikata da hukuma ta gwamnatin tarayya a nan Amurka ta ke kashewa.

Shugaba Obama yana samun albashin Dala dubu 400 a kowace shekara, kafin a cire haraji daga ciki. Kashi biyar na albashin nasa da zai sadaukar daga ranar 1 ga watan Maris, lokacin da wannan doka ta fara aiki, na nufin cewa a kowane wata zai mayar da kimanin dala dubu daya da dari bakwai.

A ranar talata ma, sakataren tsaron Amurka, Chuck Hagel, da mukaddashinsa Ashton Carter, duk sun ce su ma zasu maidawa gwamnatin wani bangare na albashinsu a matsayin wani matakin jajantawa ma'aikatansu da zasu yi hasarar wani bangare na albashinsu.
XS
SM
MD
LG