Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

A BARI YA HUCE: Labarin Malami Da Mahaukaci - Yuni,26, 2021


Alheri Grace Abdu
Alheri Grace Abdu

Wani malami ne yana koyar da darasin Hausa, bayan ya kamala bayani sai ya ce bari ya gwada ya ga ko daliban sun fahimci abinda ya koyar. Ashe bai sani ba a cikin wadanda ke zaune a ajin akwai wani mahaukaci.

Da malamin ya ce ina son idan na fadi wani abu daya daga cikin ku ya fada min kishiyar, nan da nan mahaukaci ya daga hannu ya ce zai bada amsa. Malamin ya ce sama sai Mahaukacin yace kasa, Malam yace Ruwa sai Mahaukacin yace Iska, Malam yace Wuta sai Mahaukacin yace Aljanna, Malam yace Malami sai Mahaukacin yace Dalibi, Malam yace mai kudi Mahaukacin yace Talaka, sai malamin yayi murmushi yace amma kana da kokari, sai Mahaukacin yace amma kai dakiki ne.

Malamin ya ga “dalibin” yana neman ya wuce gona da iri sai yace to ya isa haka, sai Mahaukacin yace bai isa ba, Malamin yace kana da hankali kuwa, sai Mahaukacin yace kai ma Mahaukaci ne…

Saurari shirin domin jin cikakken labarin da Hadiza Isa Wada ta aiko mana:

A Bari Ya Huce: Labarin Malami da Mahaukaci 24: 00"
please wait

No media source currently available

0:00 0:24:26 0:00


  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG