Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

A Karon Farko, Osinbanjo Ya Halarci Taron Majalisar Zartarwa A Zahiri Bayan Kammala Jinya


Farfesa Yemi Osinbajo (Facebook: Prof. Yemi Osinbajo)
Farfesa Yemi Osinbajo (Facebook: Prof. Yemi Osinbajo)

A watan Yulin da ya gabata, Osinbajo ya sanar da cewa an yi masa tiyata a kafa sanadiyyar wani ciwo da ya ce ya jima yana fama da shi.

A karon farko tun bayan da aka yi masa tiyata, Mataimakin shugaban Najeriya, Farfesa Yemi Osinbajo, a ranar Laraba ya halarci taron majalisar zartarwa a zahiri.

A watan Yulin da ya gabata, Osinbajo ya sanar da cewa an yi masa tiyata a kafa sanadiyyar wani ciwo da ya ce ya jima yana fama da shi.

Wani hoto da aka wallafa a shafinsa na Facebook a watan Yuli, ya nuna mataimakin shugaban kasar rike da sanda tare da mai dakinsa da kuma wasu ma'aikatan lafiya.

Ministoci da jami'an gwamnati, suna gaishe da Osinbajo a taron majalisar zartarwa (Facebook: Yemi Osibanjo)
Ministoci da jami'an gwamnati, suna gaishe da Osinbajo a taron majalisar zartarwa (Facebook: Yemi Osibanjo)

A lokacin da yake jinyar, mataimakin shugaban kasar kan halarci taron majalisar zartarwar ne da wasu taruka ta kafar yanar gizo.

Yayin zaman taron wanda ya gudana a fadar shugaban kasa a ranar Laraba a Abuja, an ga ministoci da sauran ma’aikatan fadar suna ta yi wa Osinbajo barka da dawowa.

Kamar yadda aka saba a duk lokacin da yake kasa, Shugaba Muhammadu Buhari ne ya jagoranci zaman majalisar zartaswar.

Tambayoyin wasu ‘yan kasashen Afirka akan manufifi da Shugabancin Donald Trump ga kasashensu
please wait

No media source currently available

0:00 0:09:10 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG