Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Adamawa: Tashin Hankali Tsakanin Fulani Makiyaya Da ‘Yan Yankin Kwateh


Shanun Fulani Makiyaya
Shanun Fulani Makiyaya

Rahotanni daga jihar Adamawa arewa maso gabashin Najeriya na cewa kimanin rayuka hudu ne aka rasa a wani sabon rikici dake neman barkewa a tsakanin Fulani Makiyaya da kabilun yankin Kwateh a yankin karamar hukumar Girei.

An tabbatar da cewa rikicin na neman tashi ne biyo bayan kashe wasu Fulani makiyaya biyu, inda suma fulanin suka kashe wasu mutanen yankin biyu a wani harin daukar fansa.

To sai dai tuni wannan lamarin yakai ga fara kona gidajen wasu Fulani makiyaya a yankin, kamar yadda shugaban karamar hukumar Girein Alhaji Hussaini Masta, ya tabbatar ta wayar talho.

To sai dai kuma, rundunar yan sandan jihar Adamawan, ta bakin kakakinta SP Othman Abubakar, ta danganta lamarin da cewa yan fashi da makami ne sukayi kisan.

A baya dai yankin yayi fama da tashe tashen hankula dake da nasaba da fadan kabilanci a tsakanin al’umomin biyu, lamarin da ya jawo asarar rayuka da dukiya, batun da ya kai kafa kwamitocin sasantawa, wanda kawo yanzu da alamun basu fara haifar da mai ido ba.

Domin karin bayani saurari cikakken rahotan Ibrahim Abdul’aziz.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:16 0:00

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG