Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Na Son A Bincike Rawar Da Iran Ke Takawa A Rikicin Yemen


Wadansu gine gine da aka kaiwa hari a Yemen
Wadansu gine gine da aka kaiwa hari a Yemen

Fadar shugaban Amurka ta White ta yi kira ga Majalisar Dinkin Duniya ta binciki irin rawar da Iran take takawa a rikicin da ake yi a Yemen, tana zargin Iran da assasa rikicin domin ta kara fadada burinta na mamayar yankin.

Saudiyya, abokiyar kawancen Amurka, ta zargi Iran da samar da makamai ga 'yan tawayen Houthi, ciki harda makami mai linzami, da saudiyyar ta tare, bayan da aka auna tashar jirgin samanta a Riyadh.

Saudiyya ce jagorar gamayyar rundunar hadin guiwa dake fafatawa da 'yan tawayen Houthi, a zaman goyon bayanta ga gwamnatin kasar, har ta fada a farkon makon cewa, matakin na Iran ana iya kallonsa a zaman "ayyana yaki akan kasar."

Sanarwar da fadar ta shugaban Amurka ta bayar a yau laraba, ta bayyana goyon baya ga kasar Saudiyya da wasu kawayenta a yankin, tana mai cewa Iran ta keta haramcin da Majalisar Dinkin Duniya ta yi mata na raba makamai.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG