Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Ta Himmatu Wajan Gurfanar Da Wadanda Sukai Yunkurin Hambare Gwamnatin Turkiyya


A nan birnin Washington ne jiya Lahadi shugaban Amurka Barack Obama ya tabbatar wa shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan cewa, Amurka ta himmantu ga batun gurfanar da duk wadanda ke da hannu a yunkurin kifar da gwamnatinsa da bai yi nasara ba a gaban shari’a, amma bai fadi cewa Amurka zata mika ma Turkiyya babban malamin da ta ke zargi ba.

A lokacin da Obama ke ganawa da shugaban Turkiyya a taron kolin manyan kasashe na G-20 yace “Zamu tabbatar da cewa duk wadanda ke da hannu sun fuskanci shari’a.”

Turkiyya dai ta tsaya kan bakarta na cewa shahararren malamin addinin Islaman nan ‘dan shekaru 75 da haihuwa Mallam Fethullah Gulen, ya na da hannu a juyin mulkin, wanda yanzu haka yake zaman hijira a jihar Pennsylvania ta Amurka, tun shekarar 1999. Sai dai Mallam Gulen, ya fito ya musanta alakarsa da juyin mulkin.

Turkiyya dai ta bukaci Amurka da ta mayar mata da Gulen, amma jami’an Amurka sunce har yanzu Turkiyyar ba ta basu wata shaidar da take nuna cewa Gulen na da alaka da yunkurin juyin mulkin da bai sami nasara ba, a kokarin hambare gwamnatin shugaba Erdogan. Amurka dai tace kafin yunkurin mayar da duk wani mutum wata ‘kasa dole ne sai an bayar da shaida kuma kotun Amurka ta amince.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG