Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Tace Zasu Ga Bayan Kungiyar ISIS


Sakataren Harkokin Wajen Amurka John Kerry
Sakataren Harkokin Wajen Amurka John Kerry

Sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry, ya baiwa Faransawa kwarin guiwar cewa "zamu samu galaba kan Daesh", sunan da ake kiran kungiyar ISIS da Larabci . Mr Kerry yayi wannan furucin ne lokacinda ya kai ziyarar jajantawa da kuma nuna goyon bayan 'yan uwantaka a kasar. Ya kuma kara da cewa "suna kan hanyar samun nasara" kan kungiyar.

An tsananta matakan tsaro lokacinda Mr. Kerry ya sauka a Paris babban birnin kasar Faransan a daren jiya Litinin. An hana 'yan jarida raka shi, matakin da ake gani shine irinsa na farko ga babban jami'i da ya kai ziyar aiki a fadar wata kasa a Turai.

Yace "kada wani yayi kokwanto har yanzu da hasken fitila tana ci a birnin da ake kira mai haske" inji Mr. Kerry. Yace "yau mu duka 'yan birnin Paris ne."

Tunda farko shugaban kasar Farncois Hollande, ya lashi takobin zafafa kai farmaki a Syria, inda daga can ne aka kitsa makarkashiyar hare haren da aka kai kan birnin. Shugaban ya gabatar da jawabin ba kasafai ba ga hadin gwiwar majalisun kasar.

Haka nan kuma a jiya Litinin, hukumomin kasar suka kama mutane 23 a sumamen da suka kai a duk fadin kasar, suna masu fadin cewa sun gano mutumin da ake zargin shine madugun shirya hare haren da aka kai kan kasar.

XS
SM
MD
LG