Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Tana Matsin Lambar Ganin Pakistan Ta Saki Jami'inta.


Shugban kasar Pakistan Asif Ali Zardari, da wata tawagar wakilan majalisar dokokin Amurka da suke ziyara cikin kasar.
Shugban kasar Pakistan Asif Ali Zardari, da wata tawagar wakilan majalisar dokokin Amurka da suke ziyara cikin kasar.

Amurka ta kara kaimin matsawa Pakistan lamba da nufin ganin an saki wani jami’in diplomasiyanta da ake zargi da harbin bindiga da ya yi sanadin mutuwar ‘yan kasar Pakistan uku.

Amurka ta kara kaimin matsawa Pakistan lamba da nufin ganin an saki wani jami’in diplomasiyanta da ake zargi da harbin bindiga da ya yi sanadin mutuwar ‘yan kasar Pakistan uku.

Jami’an kasar Amurka sun bayyana jiya Talata cewa, gwamnatin shugaba Obama tana kayyade irin huldar siyasa da take yi da Pakistan, sai dai kawo yanzu, tattaunawar da ake shirin yi ranar 24 ga wannan wata na Fabrairu tsakanin manyan jami’an Amurka da na Afghanistan da kuma Pakistan yana nan kamar yadda aka tsara.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Amurka P.J Crowley ya shaidawa Muriyar Amurka cewa, an takaita batutuwan da ake tattaunawa tsakanin manyan jami’an Amurka da kuma na Pakistan. An yi harbin ne ranar 27 ga watan janairu a arewa maso gabashin birnin Lahore.

Jami’an diplomasiyan Amurka sun ce jami’in da hukumomin kasar Pakistan suka bayyana mai suna Raymond Davis, ya harbe ya kuma kashe wadansu ‘yan kasar Pakistan biyu domin kare kanshi yayin wani yunkurin yi mashi fashi. An kashe mutum na uku lokacin da motar ofishin jakadancin ta banke shi a kan hanyarta zuwa inda aka yi harbin.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG