Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Gargadi Hukumomin Jihar Kaduna a Kan Gurfanar da Masu Tada Rikici Gaban Doka


KADUNA: Gwamna El-Rufai
KADUNA: Gwamna El-Rufai

Wata kungiyar fafutukar zaman lafiya a jihar Kaduna ta Global Peace Foundation ta yi kira ga hukuma da gabatar da duk masu tada rikici a cikin jihar gaban shari’a saboda sauran jama'a su dauki darasi. Kungiyar tace rashin hukunta masu laifi zai ba mutane daman aikata son zuciya.

Wannan kira da kungiyar tayi ya biyo ne bayan wani sabon hari da aka kai a unguwar Mailafiya ta karamar hukumar mulkin Jama’a a kudancin jihar Kaduna. Kafin wannan hari a jajibirin bukin Kirsemeti, an dauki lokaci ba a kara jin wani hari ba a kudancin Kaduna da ya saba ganin tashe tashen hankula.

Sheikh Haliru Abdullahi Maraya na kungiyar Global Peace Foundation ya nuna takaicinsa ganin babu wanda aka taba gurfanar da shi gaban doka a sanadin tashe tashen hankula da aka saba gani a jihar Kaduna. Sheikh Abdullahi yace akwai bukatar farfado da tsarin iyayen kasa wanda kafin hukuma ta dauki mataki, su wadannan masu unguwa zasu iya tsawatawa.

Shima Reverend Joseph John na Peace Foundation yace akwai bukatar shiga cikin mutane domin a jawo hankalinsu a kan muhimmancin zaman lafiya.

Babban mai magana da yawun gwamnan Kaduna, Samuel Aruwan ya jajantawa yan uwa da abokan arziki na wadanda suka mutu a cikin rikicin. Yace gwamnati zata ci gaba da yin hadin gwiwa da jami’an tsaro wurin kare lafiyar al’ummar jihar.

please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:04:08 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG