Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Gargadi ‘Yan Najeriya Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan a Landan


Iyayen Wani Yaro Dan Najeriya, Damilola Taylor Da Aka Kashe a Landan a 2006
Iyayen Wani Yaro Dan Najeriya, Damilola Taylor Da Aka Kashe a Landan a 2006

Bayan rahotannin karin kashe ‘yan Najeriya a birnin Landan, mai bai wa Shugaba Buhari shawara kan harkokin ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje, Hon Abike Dabiri-Erewa ta gargadi ‘yan Najeriya da su yi taka tsan-tsan.

A wata sanarwar da mataimakinta, Abdur-Rahman Balogun ya fitar a Abuja, Dabiri-Erewa ta ce abin damuwa ne ganin yadda ake samun karin kashe ‘yan Najeriya musamman mazauna birnin Landan.

"Yawaitar kashe bakaken fata, musamman 'yan Najeriya a Landan, ya zama babban abin damuwa" Sanarwa ta bayyana.

Rahotanni na nuni da cewa, a farkon shekarar 2018 kawai, an kashe ‘yan Najeriya sama da 50 wadanda aksarinsu matasa ne ta hanyar daba musu wuka ko kuma aka bindigesu.

Dabiri-Erewa ta shaida cewa ta isar da bukatar bi musu hakkinsu ga babban jakadan Birtaniya a Najeriya.

Wannan sanawar na zuwa ne a daidai lokacin da shugaba Buhari ke halartar taron kasashen da Ingila ta raina a birnin na London. A lokacin wannan ziyarar, ana sa ran zai gana da Firai Minista Theresa May.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG