Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Gudanar Da Gagarumar Zanga Zanga a Malawi


Masu zanga zanga a Malawi
Masu zanga zanga a Malawi

Dubun dubatan ‘yan kasar Malawi ne suka fita zanga-zanga a jiya Alhamis, domin nuna kin amincewarsu da yunkurin da wasu suke yi na baiwa masu shari’a cin hanci a kan wata shari’ar da ake yi don kalubalantar sake zaben shugaba Peter Muthirika a bara.

Mutane sun dauki wannan matakin ne bayan da babban mai shari’ar kasar ya ce an baiwa Alkalai biyar da ke sauraron karar cin hanci.

A ranar Litinin ne aka kai karar gaban hukuma mai yaki da cin hanci a kasar, abin da ya yi sanadin soma wannan zanga-zangar a manyan biranen kasar uku.

Kimanin mutane 50,000 suka taru a babban birnin kasar Lilongwe, inda wasu tsiraru kuma suka taru a birnin Blantyre da Mzuzu.

Shugabannin adawa sun ce, anyi zamba a zaben da aka gudanar a ranar 21 ga watan Mayun bara, inda Mutharika ya yi nasarar doke abokin karawarsa Lazarus Chakwera da dan tazarar da bai taka kara ya karya ba.

A watan Agusta, shugabanin adawar suka kalubalanci babbar kotun Malawi a bisa sakamakon zaben, wannan shine karon farko a Malawi da za a kalubalanci zaben shugaban kasa a kotu tun da kasar ta samu ‘yancin kai daga Birtaniya a shekara ta dubu daya da dari tara da sittin da hudu.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG