Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Gudanar Da Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Plato


Wadansu mata suna jira su kada kuri'a a runfar zabe
Wadansu mata suna jira su kada kuri'a a runfar zabe

An gudanar da zaben shugabannai da kansiloli a kananan hukumomi goma sha uku na jahar Pilato, cikin kwanciyar hankali da lumana.

Tun farko, hukumar zabe mai zaman kanta a jahar Pilato ta dakatadda zaben a Kananan hukumomin Jos ta Arewa, Jos ta kudu, Barkin Ladi da Riyom saboda matsalolin tsaro.

Zaben shine karo na biyar tun lokacin da aka shigo mulkin damokradiyya a shekara ta dubu da dari tara da tasa’in da tara.

Jami’iyu hudu ne suka shiga zaben da suka hada da ADP, GPN, APC da PDP.

Duk da shike ba a sami wata matsalar tsaro da tayi tasiri ba, an sami matsalolin rashin kai kayan zabe a rumfunan zaben cikin lokaci wanda ya sanya masu kada kuri’a basu fara zaben kan lokaci ba a wurare da dama, yayinda wadansu kuma suka bayyana cewa basu ga sunayensu ba a rajistar zabe.

Duk kokarin da Wakiliyar Sashen Hausa Zainab Babaji tayi na neman bayanin daga shugaban hukumar zabe mai zaman kanta a jahar Pilato, Mr Fabian Ntung yayin dauko wannan rahoton ya cimma tura.

Saurari cikakken rahoton.

Zaben kananan hukumomi a Plato-3:00"
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:01 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG