Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kai Karar Gwamnatin Syria Game Da Kashe Wata 'Yar Jarida


Shugaban Syria, Bashar al-Assad.
Shugaban Syria, Bashar al-Assad.

Iyalan Ba’amurkiyar nan ma’aikaciyar Jaridar Sunday Times of London Marie Colvin sun shigar da kara akan gwamnatin Syria, inda suke kukan cewa gwamnatin ta yi fako ne ta kuma kasheta a shekarar 2012.

Colvin ta mutu ne tare da wani dan jaridar daukar hoto Bafaranshe Remi Ochlik, lokacin da gwamnatin Bashar al-Assad ta yi dabarar harba makanin roka zuwa wani matsugunin ‘yan jaridu a birnin Homs da ke gundumar Bab Amr a ranar 12 ga Fabrairun 2012.

Har wasu ‘yan jarida 3 ma sun jikkata a wajen. Wata kungiyar rajin kare ‘yan jaridu a birnin New York tace, gwamantin Syria ta kashe su ne saboda kar su tona asirin kanshin mutuwar da aka yi aka kashe mutane a Homs.

Ministan yada labaran kasar Syria yace, a lokacin da abin ya faru, gwamnatin ba ta ma san Colvin da Ochlik suna kasar ba.

An dai shigar da wannan karar ne a madadin ‘yar uwar Marie da ake kira Cathleen Colvin da sauran iyalansu a shekaran jiya Asabar, a babbar kotun Amurka da ke nan birnin Washington DC.

XS
SM
MD
LG