Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kama Matan da Ake Zaton Su Suka Kashe Kim Jong Nam


Kim Jong Nam yayan shugaban Kriya ta Arewa wanda aka kashe a Malaysia a hannun hagu
Kim Jong Nam yayan shugaban Kriya ta Arewa wanda aka kashe a Malaysia a hannun hagu

Da taimakon naurar daukan hoto dake filin saukar jiragen sama na kasa da kasa a birnin Kuala Lumpur na kasar Malaysia, 'yan sandan kasar suka matan da ake zargin suna da hanu a kisan dan uwan shugaban Korea ta Arewa.

A yau Alhamis, 'yan sanda a Malasiya,sun ce sun kama mace ta biyu dangane da kashe Kim Jong Nam, wanda dan'uwan ne ga shugaba Kim Jong Un.

Hukumomi sun bayyana matar a matsayin Siti Aisha, 'yar shekaru 25 da haihuwa, wadda su ka ce ta na da fasfo din kasar Indonesiya, kuma daga hotunan da nu'arar daukan hoto ta dauka a filin jigrin sama taka samu nasarar cafke ta..

Kamun na ta ya biyo bayan kamun wata matar kuma da aka yi a filin Jirgin saman kasa da kasa na Kuala Lumpur a Malasiya.

'Yan sanda sun bayyana ta da Doan Thi Huong, wacce ke tafe da takardun izinin tafiya na kasar Vietname.

XS
SM
MD
LG