Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Mayar Da Wasu ‘Yan Najeriya 326 Gida Daga Kasar Libya


Wasu 'Yan Najeriya Da Aka Dawo Da Su Daga Libiya
Wasu 'Yan Najeriya Da Aka Dawo Da Su Daga Libiya

Hukumar bada agajin gaggawa ta kasa tare da hadin gwiwar hukumar tallafawa yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta dawo da wasu yan Najeriya 326 daga kasar Libya ta babban filin jiragen sama na Murtala Muhammed dake Legas.

Karo na biyu Kenan da a ake dawo da yan Najeriya daga kasar Libya, domin ko a ranar 15 ga watan jiya saida wani jirgi ya mayar da wasu yan Najeriya 150 daga Libya.

Alhaji Idris Abubakar Muhammed dake zama babban Jami’in hukumar ta NEMA, wanda ke kula da shiyar Legas yayi karin haske game da yan Najeriyan da aka mayar da su gida. Inda ya ce sun karbi ‘yan Najeriyan ne karkashin wani shiri na gwamnatin tarayyar Najeriya.

Aksarin yan Najeriyar da ake dawowa da su dai suna zuwa kasar ta Libya ne da zummar ketarawa zuwa Turai domin samun ingantacciyar rayuwa, abin da kesa wasu rasa rayukansu tun a cikin hamadar sahara, wasu kuma su fada hannun masu fataucinn mutane da cinikin bayi.

Wasu 'Yan Najeriya Da Aka Dawo Da Su Daga Libiya
Wasu 'Yan Najeriya Da Aka Dawo Da Su Daga Libiya

Yawancin lokuta dai hukumomi na bada shawarwari da kuma daukan matakai na hana kwararan yan gudun hijiran zuwa Turai, amma alamu sun nuna cewar basa jin kira.

Domin cikakken bayani saurari rahotan Babangida Jibrin.

please wait

No media source currently available

0:00 0:04:06 0:00

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG