Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Sake Tuhumar Omoyele Sowore, Da Hada Taro Ba Bisa Ka'ida Ba


Kotu ta sake tura Omoyele Sowore, gidan jiran hukunci, akan zargin shi na tada zaune tsaye.

Wata Kotun majistare a Abuja ta tura dan jaridar nan kuma dan rajin tabbatar da demokaradiyya, Omoyele Sowore, ma'adana a gidan yarin Kuje gabanin duba bukatar ba da belin sa.

Sowore wanda shi ne mawallafin jaridar yanar gizo ta Sahara Reporters, kazalika ya jagoranci zanga-zangar juyin juya hali da 'yan sanda su ka zarge shi da yunkurin kifar da gwamnati ko cin amanar kasa.

Wannan karo 'yan sanda sun kama Sowore da gurfanar da shi gaban kotu don zarginsa da tada fitina da gudanar da haramtaccen taro.

"Wani ya na kiran a sauya gwamnati da halin makarkashiya, ba tare da bin tanadin tsarin mulki ba" inji lauyan bangaren shigar da kara James Idachaba.

Lauyan Sowore mai suna Marshal Abubakar ya ce, Sowore ya shiga kare masu zanga-zanga yayin da ya ga a na dukan daya daga cikinsu a yankin Gudu da ke Abuja.

"A lokacin da Sowore ya ke sa baki don dakatar da cin zarafin mutumin, sai jami'ar 'yan sanda DSP Altine Daniel, ta yi dirar mikiya a kan sa har da fasa ma sa hanci." Inji Marshal Abubakar.

Lauyan ya cigaba da cewa an kai su Sowore ofishin jami'an SARS da a ka soke a ka cigaba da azabtar da su.

Sowore, ya zargi gwamnatin Buhari da cin zalin sa ya na mai cewa ya gano ma har yanzu ba a rushe rundunar SARS ba.

"Lokacin da a ka kai mu ofishin tsare mutane na Abatuwa, na gano gwamnati ba ta rushe SARS ba, don sun tattaro 'yan SARS su ka doke mu da tura mu dakin tsare mutane."

Alkalin kotun Mabel Segun Bello ya tsayar da Talatar nan don duba neman belin Sowore.

Ga rahoton Nasiru Adamu El-Hikaya a cikin sauti.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:04 0:00

Karin bayani akan: Najeriya​, SARS, Omoyele Sowore, da Nigeria.

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG