Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Aung San Suu Kyi Zata Kai Ziyarar Farko A Rohingya Bayan Hare Haren Da Sojoji Suka Kaiwa Musulmi


 Aung San Suu Kyi
Aung San Suu Kyi

Shugabar Myanmar Aung San Suu Kyi ta tafi jihar Rakhine ta arewa inda aka yi fama da tashin hankali, karon farko tunda rundunar soji ta kaddamar da hari kan Musulmin Rohingya tsirarru.

Kakakin Aung San Suu Kyi yace tana kan hanyar zuwa lardin Maungdaw dake kan iyaka daga Sittwe, babban birnin jihar Rakhine inda ta isa yau da safe.

Mayakan Rohingya sun kai hari kan ofisoshin ‘yan sanda a Myanmar a watan Agusta, abinda ya sa sojoji suka kaddamar da hari a kauyukan Rohingya da ya haifar da kaurar mutane dubu dari shida daga Rakhine zuwa Bangladash, galibinsu suka yi tururuwa zuwa Cox’s Bazar. Kimanin kashi sittin cikin dari na ‘yan gudun hijiran kananan yara ne.

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyan harin da aka kaiwa Musulmin Rohongya a matsayin kisan kare dangi.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG