Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Babban kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya zai ci gaba da tattaunawa domin yin Allah wadai kan gallazawa bil'dama da gwamnatin kasar Syria ke yi


Motocin aikin soji a birnin Hama, Syria.
Motocin aikin soji a birnin Hama, Syria.

A yau Talata ne babban kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya zai dawo ya ci gaba da muhawara akan wani kuduri da ake neman a zartas na yin Allah-waddai akan gallazawar da gwamnatin Syria ke yi wa al’ummarta, musamman masu yi mata zanga-zangar nuna mata kyama.

A yau Talata ne babban kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya zai dawo ya ci gaba da muhawara akan wani kuduri da ake neman a zartas na yin Allah-waddai akan gallazawar da gwamnatin Syria ke yi wa al’ummarta, musamman masu yi mata zanga-zangar nuna mata kyama. Yau ne ake shiga rana ta biyu da soma wannan muhawara akan matakin da shugaban Syria din, Bashar al-Assad yake dauka na tura ma’aikatansa na tsaro suna fattatakar dimbin mutanen dake tarukkan zanga-zangar nuna wa gwamnatinsa kyama. Mazauna garin Hama sunce a jiya ma tankunan sojan sun sake dawowa garin, kwana guda bayanda harbe-harben da sojoji suka yi a garin. kampanin dillacin labarum Reuters ya ruwaito wasu mazauna garin na cewa an kashe akalla mutane ukku a lokacin da sojan na gwamnati suka bude wuta akan garin na Hama. Duka-duka mutane kamar ishirin da hudu aka hallaka a irin wadanan hare-haren da soja suka kai a sassan kasar daban-daban jiya Litinin. A halin yanzu kuma, Syria ta fama da matsin-lambar kasashen duniya da dama dake kira akanta da ta daina wannan fatattakar da take wa al’ummarta, abinda ya janyo har kasar Italiya ta janye jakadanta dake kasar a yau. Ita ma Sakatariyar Harkokin Wajen Amurka Hillary Clinton, a yau take shirin ganawa da wasu ‘yan hankoron neman-chanji na Syria a nan Washington, yayinda Kungiyar tarayyar Turai ta dada saka takunkumin hana tafiye-tafiye da kuma cafke kadarorin karin wasu mukrrabai biyar na gwamnatin Syria, ciki har da ministanta na tsaro, Ali Habib Mahmud.

XS
SM
MD
LG