Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Barazanar Mali Da Burkina Faso Kan Shirin ECOWAS A Nijar Ba Ta Da Tasiri -Mai Sharhi Kan Sha’anin Tsaro


Taron (ECOWAS) a Abuja, Nigeria, Aug. 2, 2023.
Taron (ECOWAS) a Abuja, Nigeria, Aug. 2, 2023.

Manazarta sha’anin tsaro na ci gaba da bayyana matsayinsu dangane da barazanar amfani da karfi da kungiyar CEDEAO ta yi wa sojojin Nijer akan bukatar su mayar da hambararen shugaba Mohamed Bazoum kafin cikar wa’adin mako daya.

Da suke maida martani kan ikirarin na ECOWAS , kasashen Mali da Burkina Faso sun lashi takobin kai dauki wa sojojin da suka yi juyin mulkin a Nijer muddin kungiyar ta kasashen yammacin Afrika ta yi amfani da karfin soja wajen warware wannan rikici.

To sai dai kamar yadda za a ji a tantaunawarsu da wakilin muryar Amurka, Souley Moumouni Barma, mai sharhi kan sha’anin tsaro Dr Seidik Abba na ganin Mali da Burkina Faso ba su da karfin da zai ba su damar taka wata babbar rawa idan aka yi katari CEDEAO ta zartar da kudirinta kan sojojin na Nijer.

Saurari hirarsu a sauti:

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:33 0:00

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG