WASHINGTON, DC —
Kungiyar kwallon kafar Bayer Leverkusen ta Jamus ta sallami kwach din ta Sami Hyypia a yau asabar din nan, a bayan da ta fuskanci kalubale sosai a wasanninta na baya-bayan nan, kuma a yanzu ma tana fuskantar barazanar zamewa daga matsayi na 4, abinda zai hana ta samun shiga gasar cin kofin zakarun kulob na Turai a shekara mai zuwa.
An nada kwach na kungiyar matasan kulob din, Sascha Lewandowski, ya rike Leverkusen har zuwa karshen kakar kwallo ta bana.
Leverkusen ta sallami kwach din nan take, a bayan da jiya jumma’a ta sha kashi a hannun Hamburg SV wadda take can kasa a teburin Bundesliga, inda a yanzu Wolfsburg da Borussia Moenchengladbach su na iya shige ture ta daga matsayi na 4 a wasannin da zasu yi yau asabar.
A farko farkon wannan kakar kwallo, Leverkusen ita ce ta biyu a teburin Bundesliga, amma a wasanni 12 na bayan nan da ta yi, kwaya 3 kawai ta samu nasarar lashewa. Haka kuma ta sha kashi sosai a hannun PSG ta Faransa a gasar cin kofin zakarun kulob na Turai da kuma Kaiserslautern a gasar cin kofin kalubalenka na Jamus.
An nada kwach na kungiyar matasan kulob din, Sascha Lewandowski, ya rike Leverkusen har zuwa karshen kakar kwallo ta bana.
Leverkusen ta sallami kwach din nan take, a bayan da jiya jumma’a ta sha kashi a hannun Hamburg SV wadda take can kasa a teburin Bundesliga, inda a yanzu Wolfsburg da Borussia Moenchengladbach su na iya shige ture ta daga matsayi na 4 a wasannin da zasu yi yau asabar.
A farko farkon wannan kakar kwallo, Leverkusen ita ce ta biyu a teburin Bundesliga, amma a wasanni 12 na bayan nan da ta yi, kwaya 3 kawai ta samu nasarar lashewa. Haka kuma ta sha kashi sosai a hannun PSG ta Faransa a gasar cin kofin zakarun kulob na Turai da kuma Kaiserslautern a gasar cin kofin kalubalenka na Jamus.