Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

BELGIUM: An Soke Bukin Sabuwar Shekara Bisa Dalilan Tsaro


A Belgium, magajin Brussels, babban birnin kasar, ya soke bikin shekara-shekara na shigar sabuwar shekara na bana, saboda an sami rahotanni kanbarazanar ta'addanci.

Magajin garin, Yvan Mayeur, wanda yayi magana da kafofin yada labaran kasar, yace, cibiyar da take nazarin bala'o'i, tace da wuya a tantance dubun dubatan mutane da zasu hallara a dandalin bukukuwan shiga sabuwar shekarar.

A farkon makon nan 'Yansandan kasar, suka kama mutane biyu kan zargin suna shirya makarkashiyar harin ta'addanci, kan abunda jami'an tsaron suka kira cibiyoyi na tarihi ko masu muhimanci. Masu gabatar da kara a gaban kotu, sun kira barazanar a zaman "mai tsanani."

Hudu daga cikin maharan da suka kai farmaki a birnin Paris cikin watan Nuwamba, 'yan kasar Belgium ne.

Ahalinda ake ciki kuma, dubban 'Yansanda ne wasu dauke dogayen bindigogi, da na'urorin gano makamai masu guba da ire-irensu, da karnuka masu iya gano abubuwa, suna daga cikin gungun jami'an tsaro da zasu samar da tsaro a dandalin Times dake birnin New York, a bukin shigar sabuwar shekara, da za'a yi can anjuma da dare.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG