Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

China Tayi Barazanar Watsi Da Matsayar Cinikayya Da Amurka


Kasar China ta gargadi Amurka cewa, ba za a aiwatar da duk wata matsayar cinikayya da aka acimma tsakanin kasashen biyu ba, muudar aka kara kudin fito da kuma daukar wadansu matakan da shugaba Donald Trump ya yi barazana a kan China.

China tayi wannan gargadin ne bayan ganawar sakataren harkokin kasuwanci na Amurka Wilbur Ross da mataimakin Firai Ministan kasar China Liu He a Beijing jiya asabar da nufin dinke barakar harkokin cinikayya tsakanin kasashen inda Beijing ta yi alkawarin rage rarar da ake samu a harkokin cinikayyarta.

Ross ya fada a farkon tattaunawar da aka yi a gidan baki na gwamnati dake Diaoyutai, kasashen biyu sun tattauna musamman kan kayyakin Amurka da China zata saya, sai dai an tashi tattaunawar ba tare da wata sanarwar hadin guiwa ba, kuma babu wani daga cikin bangarorin da ya yi wani Karin haske a kan tattaunawar.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG