Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Daga Karshe An Ceto Bakin Hauren Nan Da Suka Makale A Teku


Bakin Haure A Italiya

Bakin haure sama da 80 da ke cikin jirgin ruwan nan na kasar Spain da ya cecesu a kan teku, sun taka doron kasa a karon farko, bayan da suka kwashe kwanaki 20 a cikin jirgin da ya yi ta galantoyi akan teku.

Lamarin ya faru ne bayan da hukumomin Italiya suka kwace jirgin mai suna “Open Arms” wanda ke ayyukan jinkai na kubutar da bakin hauren da su ka makale akan teku.

Andre Mahecic, shi ne kakakin hukumar da ke kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya, ya kuma ce “Akwai bukatar a tallafa musu, domin ganin sun koma cikin hayyacinsu, saboda an ci zarafin aksarinsu cikin watannin da suka kwashe a kasar Libya.”

Bakin hauren dai sun barke da shewa, a lokacin da suka ji labarin cewa hukumomin Italiya sun kwace jirgin.

Facebook Forum

An Sami Karuwar Farashin Kayayyaki A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:42 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Shiye-Shiryen Shiga Watan Azumi A Kasar Ghana
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:56 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Ziyarar Sakatare Blinken A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Al'umomi Sun Koka Game Da Tashin Farashin Kayayyaki
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG