Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Dakarun Isra'ila Sun Kai Hari Syria


Ministan Tsaron Isra'ila Gilad Erdan
Ministan Tsaron Isra'ila Gilad Erdan

Tun lokacin da rikicin Syria ya barke a shekarar 2011 ne dakarun Israila suke kai hari cikin Syria jefi jefi domin dakile duk wani kokarin kaiwa kungiyar Hezbollah makamai a Lebanon.

Sojojin Syria sun ce dakarun Israila sun harba nakiyoyi yau Talata da suka doshi yankin kasar a wani bangaren Arewacin Damaskas.

Sojojin sun ce sun harba wasu nakiyoyin kafin su fashe, yayin da wasu suka ruguza wani yankin da ke kusa da sansanin sojoji a Quetayfeh.

Sanarwar Sojin ta bayana cewa dakarun Syria sun harbo wani Jirgin saman Israila a wani mayar da martani

Sai dai dakarun Israila din sun ki bada wani bayani. Da ma Israila ta sha kai hare hare tun da aka fara samun tashin hankali a shekarar 2011 ba tare da fitowa fili ba.

Jami’an Israila sun tabbatar da cewa hare haren da suka kai a baya sun yi ne domin makamai masu yawa da suke zaton za a kai sansanin ‘yan ta’addar Hezbollah da ke Lebanon ne.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG