Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Sa Dangote a Jagororin Kwamitin Farfado Da Arewa Maso Gabashin Najeriya


Attajirin Afirka,Aliko Dangote.
Attajirin Afirka,Aliko Dangote.

Gwamantin Najeriya ta kafa kwamitin farfado da suman jihohi irin su Borno da Yobe sakamakon hare-haren ta'addancin 'yan kungiyar Boko Haram.

Sannin jama'a ne cewa, hare-haren ta'addanci da yaki da 'yan Boko Haram yayi dai dai da jihohin Arewa maso Gabashin Najeriya kamar irin su Borno da Yobe.

Wannan ne yasa gwamnatin tarayyar Najeriya a karkashin shugabancin Shugaba Muhammadu Buhari, inda ya nada Janar TY Danjuma mai ritaya da Aliko Dangote a matsayin wadanda zasu jagoranci kwamitin da aka kafa don farfado da yankin da abin ya shafa.

Mutane da dama suna ganin ai bai dace a ba wadannan attajiran wannan aikin ba, ka abin ya zama wani jirwaye mai kamar wanka. To wasu kuwa gani suke ai haka ne ya fi dacewa da su.

Domin suna ganin kasancewarsu masu arziki ba zasu yi wadaka da dukiyar kasa da suna gyara jihohin ba, hasali ma dai sai dai su yi amfani kila da nasu kudin wajen inganta raya yankunan. Ga

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:17 0:00


XS
SM
MD
LG