Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Firayim Ministan Kasar Mali Da Mambobinsa Sunyi Ritaya


Firayim Ministan kasar Mali Soumeylou Boubeye Maiga da dukan mambobin gwamnatinsa sun yi murabus a jiya Alhamis.

Wata sanarwa daga ofishin shugaban kasar Ibrahim Boubacar Keita ta ce: "Shugaban kasa ya amince da murabus din na firaministan kasar da na mambobin gwamnatin sa."

Wannan mataki ya zo ne bayan tashe tashen hankula a yankin tsakiyar kasar, ciki har da kisan gilla a watan jiya na Fulani 160, wanda ake zargin mafarauta na Dogon ne suka aikata.

Majalisar Dinkin Duniya ta fitar rahoton cewa, a cikin shekarar da ta wuce, fada tsakanin Fulani da al’umar Dogon ya janyo mutuwar mata da yara da maza har guda 600.

Makonni biyu da suka wuce an yi zanga-zanga a garin Bamako, babban birnin kasar, don nuna rashin amincewa da rashin ikon gwamnati na hana aukuwar tashe tashen hankula.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG