A ci gaba da nazarin hanyoyin shawo kan sace al'umma da kare hakkokin bil'adama, yau shirin Domin Iyali ya yada zango a birnin tarayya Abuja inda Sashen Hausa ya hada kan masu ruwa da tsaki domin neman hanyar shawo kan sace sacen kananan yara biyo bayan kwato wadansu kananan yara tara da aka sace a birnin Kano aka kai Anambra inda aka canza masu sunaye da addini.
Taron ya sami halartar jami'an 'yan sanda, shugabannin addinai, kungiyoyi masu zaman kansu, 'yan gwaggwarmaya da sauran masu ruwa da tsaki daga ciki da wajen Abuja.
Saurari kashin farko na tattaunawar.
-
Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.